fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƴan ta’adda sun jefa bam ofishin ƴan sandan Kogi

Date:

Wasu ‘yan bindiga da sanyin safiyar Juma’a sun kai harin bam a ofishin ‘yan sanda da ke Eika-Ohizenyi a karamar hukumar Okehi a jihar Kogi, inda suka kashe wani sufeto Jibril da ke bakin aiki.

Wani mazaunin yankin, Malam Momoh Abubakar, ya bayyana cewa, maharan sun mamaye wajen ne da misalin karfe 12:15 na safe dauke da bama-bamai da sauran makamai.

Ya bayyana cewa, bam na farko da suka jefa a cikin ofishin ya yi wani kara mai karfi da ta tada da yawa mazauna wurin, inda ya kara da cewa , bama-baman da suka tayar da wani bangare na ofishin ‘yan sandan.

Abubakar ya kara da cewa, maharan sun samu ranar, domin sun shafe sama da sa’o’i biyu suna gudanar da ayyukansu ba tare da tsangwama daga jami’an tsaro ko jama’ar gari ba.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kogi, Edward Egbuka, ya ce, ya ba da umarnin tura karin kadarorin aiki, wadanda suka hada da jami’an rundunar ‘yan sanda na sashin yaki da ta’addanci, sashin amsa gaggawa, ofishin leken asiri na jihar tare da hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro don dawo da zaman lafiya yankin. In ji Daily Trust.

A cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP William Aya, wani bangare na ofishin rundunar ‘yan sandan yankin ya kone kurmus da maharan suka yi amfani da su.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp