fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƴan ta’adda sun jefa bam ofishin ƴan sandan Kogi

Date:

Wasu ‘yan bindiga da sanyin safiyar Juma’a sun kai harin bam a ofishin ‘yan sanda da ke Eika-Ohizenyi a karamar hukumar Okehi a jihar Kogi, inda suka kashe wani sufeto Jibril da ke bakin aiki.

Wani mazaunin yankin, Malam Momoh Abubakar, ya bayyana cewa, maharan sun mamaye wajen ne da misalin karfe 12:15 na safe dauke da bama-bamai da sauran makamai.

Ya bayyana cewa, bam na farko da suka jefa a cikin ofishin ya yi wani kara mai karfi da ta tada da yawa mazauna wurin, inda ya kara da cewa , bama-baman da suka tayar da wani bangare na ofishin ‘yan sandan.

Abubakar ya kara da cewa, maharan sun samu ranar, domin sun shafe sama da sa’o’i biyu suna gudanar da ayyukansu ba tare da tsangwama daga jami’an tsaro ko jama’ar gari ba.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kogi, Edward Egbuka, ya ce, ya ba da umarnin tura karin kadarorin aiki, wadanda suka hada da jami’an rundunar ‘yan sanda na sashin yaki da ta’addanci, sashin amsa gaggawa, ofishin leken asiri na jihar tare da hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro don dawo da zaman lafiya yankin. In ji Daily Trust.

A cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP William Aya, wani bangare na ofishin rundunar ‘yan sandan yankin ya kone kurmus da maharan suka yi amfani da su.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...
X whatsapp