fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƴan majalisar dokokin Oyo PDP za su sauya sheƙa zuwa APC

Date:

‘Yan majalisar dokokin jihar Oyo takwas da aka zaba a karkashin jam’iyyar PDP za su fice daga jam’iyyar.

An tattaro cewa, ‘yan majalisar da wasu jiga-jigan jam’iyyar a jihar Kudu maso Yamma sun kammala shirin komawa jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Naija News ta tuna cewa, a baya-bayan nan ne mataimakin gwamnan jihar Oyo, Rauf Olaniyan ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC, bayan da suka samu sabani da gwamna Seyi Makinde.

Makinde, wanda ke neman sake tsayawa takara a 2023, ya ki ya zabi Olaniyan a matsayin abokin takararsa.

Daya daga cikin ‘yan majalisar PDP da suka fusata ya tabbatar da cewa, wasu ‘yan majalisar na shirin ficewa daga jam’iyyar mai mulki ranar Lahadi.

Ya shaida wa Vanguard cewa, shirin sauya shekar ya kasance ne, saboda an hana ‘yan majalisar dokokin jihar tikitin tsayawa takara a zaben 2023 na PDP.

A halin da ake ciki kuma, an yi Allah wadai da Shugaban Jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu, da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Atiku Abubakar, kan kin kamfe na jam’iyyar a Ekiti.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp