fidelitybank

Da Ɗumi-Ɗumi: Ƴan bindiga sun kashe shugaban Miyetti Allah

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari tare da kashe shugaban kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders’ Association of Nigeria (MACBAN), Adamu Aliyu a unguwar Gwagwalada da ke Abuja.

An kashe Aliyu ne tare da wasu mutane hudu a kusa da kauyen Daku da ke gundumar Dobi ta karamar hukumar a ranar Alhamis.

Mohammed Usman, Sakataren MACBAN, yayin da yake tabbatar da kisan shugaban, a ranar Lahadi ya ce, an kuma yi garkuwa da mutane uku.

A cewar Usman, wasu uku sun jikkata kuma an kai su asibiti. Ya ce, marigayi shugaban MACBAN da wasu mutane shida suna dawowa ne daga Kasuwar Izom ta Jihar Neja, lokacin da aka kai masa hari.

“Suna dawowa daga Kasuwar Izom da ke Jihar Neja inda suka je sayar da shanu, sai da ya kai kilomita daya kacal zuwa kauyen Daku, kwatsam ‘yan fashin sun fito daga daji suka bude wa motar wuta, inda suka kashe shugaban MACBAN da wasu hudu,” inji shi. .

Ya bayyana sunayen wadanda aka kashen a matsayin Saleh, Aliyu, Muhammadu da Saidu, yana mai cewa an binne su kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Ya ce, jami’an tsaro suna nan a wurin kafin a yi jana’izar marigayin.

Shima shugaban karamar hukumar Gwagwalada Alhaji Adamu Mustapha ya tabbatar da faruwar lamarin.

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp