fidelitybank

Cutar Ƙyandar biri ta ɓulla a sansanin gudun hijira a Borno

Date:

Bayanai daga birnin Maiduguri na jihar Borno na cewa an samu ɓullar cutar ƙyandar biri a ɗaya daga cikin sansanonin da aka tsugunar da mutanen da ambaliya ruwa ta raba da muhallansu.

Cikin wata sanarwa da hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasar NEMA, ta fitar ta ce tawagar jami’an lafiyarta tare da tallafin ma’aikatan Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO da na hukumar raya ƙasashe ta Amurka da, USAID sun samu nasarar keɓe wadda ake zargi ta kamu da cutar tare da mahaifiyarta da kuma mutanen da ake kyautata zaton sun yi mu’alama da marar lafiyar.

Mahaifiyar yarinyar ta bayyana cewa ‘yar tata ta fara fitar da ƙuraje a jikinta tsawon mako biyu da suka gabata, sai dai babu wani daga cikin ‘yan uwanta da ya nuna alamun cutar.

Tuni hukumomin lafiyar jihar suka ɗauki samfurin jininta domin faɗaɗa bincike, yayin da take ci gaba da samun kulawar likitoci.

Hukumar ta NEMA ta kuma ce tuni suka sanar da hukumomin da lamarin ya shafa, ciki har da hukumar daƙile yaɗuwar cutuka ta NCDC.

Haka kuma hukumar ta NEMA, ta umarci mutane da ɗauki matakan kariya domin daƙile yaɗuwar cutar a cikin sansanin, ciki har da yawaita wanke hannu da tsaftace muhallin.

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp