fidelitybank

Cutar Mashaƙo ta bulla a Abuja

Date:

Hukumar kula da babban birnin tarayya, Abuja ta sanar da bullar cutar mashaƙo ko kuma diphtheria a wasu sassan birnin.

Jaridar Punch ta ruwaito daraktan sashen kula da lafiyar jama’a a hukumar, Dakta Sadiq Abdulrahman yana sanar da ɓullar cutar.

Abdulrahman ya ce tuni cutar ta kashe wani yaro ɗan shekara hudu, inda ya kara da cewa ɓullar ta tun farko a jihohin Legas da Ondo da kuma Kano a watan Janairu, cutar ta sanya cibiyar yaƙi da cutuka (NCDC) ta Najeriya kai ɗauki a matakin ƙasa gaba ɗaya.

Diphtheria, cuta ce da ke janyo ƙwayoyin cuta masu guba kuma suna sarƙe numfashi, da janyo matsalolin bugun zuciya, har ma suna iya kaiwa ga mutuwa.

Daraktan ya ce an tabbatar da bullar cutar ne bayan gwaje-gwajen da aka yi wa samfuran wadanda ake zargin sun kamu a wani yanki da ke kusa da Dei-Dei.

“Makonni biyu da suka wuce, mun samu bayanai daga wani yanki na birnin Abuja inda aka yi zargin mutum takwas na ɗauke da alamomin cutar kuma hakan ya sa hukumarmu ta dauki samfuran wasu mutane.

Ya buƙaci mazauna yankin su bayar da rahoton duk wani baƙon alamu, musamman kalubalen numfashi ga hukumomin da abin ya shafa kuma ya shawarci su kula da tsaftar jiki da ta muhalli.

Abdulrahman ya ce hukumarsu na hada kai da jihohi makwabta, domin daƙile yaɗuwar cutar ta hanyar sanya ido kan iyakoki.

Haka kuma, babban sakataren hukumar lafiya matakin farko na Abuja, Dokta Yahaya Vatsa, ya yi gargadin cewa mutanen da ba a yi musu alluran riga-kafi ba wadanda ke zaune a wurare masu cunkoso da rashin tsafta na cikin hatsarin kamuwa da cutar mashaƙon.

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp