fidelitybank

Cutar Mashako ta yi ajalin Yara hudu a Kano

Date:

Rahotanni na cewa cutar mashaƙo wadda aka fi sani da Diphtheria a turance, ta yi sanadiyar mutuwar yara huɗu yan gida ɗaya a unguwar Hotoron Yan Dodo, dake ƙaramar hukumar Tarauni a jihar Kano.

Rahotonni sun bayyana cewa lamarin ya faru a cikin makonni biyu.

Mahaifin yaran, Malam Yusuf Maitama, ya bayyana cewa ƙaddarar ta fara ne da ƙaramin ɗansa mai ƙasa da shekaru biyar, wanda ya fara fama da zazzaɓi da ciwon maƙogwaro kafin daga bisani ya rasu. Bayan haka kuwa, sauran uku daga cikin ‘ya’yansa suka nuna irin waɗannan alamomin, duk da ƙoƙarin ceto su, amma sun rasu, sai babbar ‘yarsa ce kaɗai ta tsira bayan an kai ta asibiti cikin gaggawa. Kamar yadda jaridar Daily News 24 Hausa ta rawaito.

Rahotanni sun nuna cewa yaran sun nuna alamomin cutar ta mashaƙo irin su zazzaɓi mai zafi da ciwon maƙogwaro.

Bayan faruwar lamarin, jami’an lafiya sun kai ziyara gidan, inda suka tsaftace muhallin tare da yi wa sauran yara rigakafin cutar a unguwar, domin hana yaduwar ta.

Gwamnatin jihar Kano ta ce ta ware asibiti na musamman domin kula da masu fama da cutar, tare da tabbatar da cewa ana bayar da rigakafi da magani kyauta ga dukkan yara. Haka kuma ta yi kira ga iyaye da su tabbatar da yin rigakafin yara da kuma gaggauta kai su asibiti idan aka fara samun alamomin cutar.

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp