Jamiāar sadarwa ta UNICEF a Najeriya, Ms Safiya Akau, a ranar Alhamis, ta ce cutar mashako ta yi ajalin rayukan yara 122 a Najeriya har zuwa watan Yulin 2023.
UNICEF a cewarta, tana kara kokarinta na dakile bullar cutar diphtheria da ta addabi yara a jihohi 27 na Najeriya.
Akau ya nakalto Ms Cristian Munduate, Wakilin UNICEF a Najeriya na cewa, āDiphtheria cuta ce mai tsanani da nauāin kwayoyin cuta da ake kira Corynebacterium diphtheriae ke haifar da guba.
“Yana iya haifar da wahalar numfashi, matsalolin bugun zuciya, da mutuwa.”
Ta kara da cewa yakan shafi mabobin hanci da makogwaro.
Akau ya bayyana cewa an tabbatar da mutane 1,387 daga cikin wadanda suka kamu da cutar diphtheria daga cikin mutane 3,850 da ake zargin sun kamu da cutar a watan Yuli.
Jamiāin sadarwa na UNICEF ya bayyana cewa Jihohi irinsu Kano, Yobe, Katsina, Lagos, Sokoto, Zamfara da FCT na fama da cutar diphtheria kuma sune kashi 98 cikin 100 na wadanda ake zargi.
Ta lura cewa yara masu shekaru tsakanin shekaru biyu zuwa 14 sun kai kashi 71.5 na wadanda aka tabbatar.
Ta ce abin takaici ne ganin cewa kashi 22 cikin 100 na wadanda aka tabbatar sun samu allurar rigakafin yara na yau da kullum.