fidelitybank

Cutar Mashaƙo ta bulla a Abuja

Date:

Hukumar kula da babban birnin tarayya, Abuja ta sanar da bullar cutar mashaƙo ko kuma diphtheria a wasu sassan birnin.

Jaridar Punch ta ruwaito daraktan sashen kula da lafiyar jama’a a hukumar, Dakta Sadiq Abdulrahman yana sanar da ɓullar cutar.

Abdulrahman ya ce tuni cutar ta kashe wani yaro ɗan shekara hudu, inda ya kara da cewa ɓullar ta tun farko a jihohin Legas da Ondo da kuma Kano a watan Janairu, cutar ta sanya cibiyar yaƙi da cutuka (NCDC) ta Najeriya kai ɗauki a matakin ƙasa gaba ɗaya.

Diphtheria, cuta ce da ke janyo ƙwayoyin cuta masu guba kuma suna sarƙe numfashi, da janyo matsalolin bugun zuciya, har ma suna iya kaiwa ga mutuwa.

Daraktan ya ce an tabbatar da bullar cutar ne bayan gwaje-gwajen da aka yi wa samfuran wadanda ake zargin sun kamu a wani yanki da ke kusa da Dei-Dei.

“Makonni biyu da suka wuce, mun samu bayanai daga wani yanki na birnin Abuja inda aka yi zargin mutum takwas na ɗauke da alamomin cutar kuma hakan ya sa hukumarmu ta dauki samfuran wasu mutane.

Ya buƙaci mazauna yankin su bayar da rahoton duk wani baƙon alamu, musamman kalubalen numfashi ga hukumomin da abin ya shafa kuma ya shawarci su kula da tsaftar jiki da ta muhalli.

Abdulrahman ya ce hukumarsu na hada kai da jihohi makwabta, domin daƙile yaɗuwar cutar ta hanyar sanya ido kan iyakoki.

Haka kuma, babban sakataren hukumar lafiya matakin farko na Abuja, Dokta Yahaya Vatsa, ya yi gargadin cewa mutanen da ba a yi musu alluran riga-kafi ba wadanda ke zaune a wurare masu cunkoso da rashin tsafta na cikin hatsarin kamuwa da cutar mashaƙon.

tribune news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp