Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa ta Najeriya NCDC ta ce, zazzabin Lassa ya kashe tare da ma’aikatan lafiya 45 da suka kamu da cutar tsakanin watan Janairu zuwa Maris.
Hukumar NCDC, a shafinta na internet da aka tabbatar a ranar Juma’a, ta kuma bayar da rahoton cewa, mutane 3,079 da ake zargin sun kamu da cutar zazzabin Lassa ne a fadin kasar, inda 630 aka tabbatar sun kamu da cutar.
NCDC ta ce, kasashen da ke makwabtaka da su na cikin hadari saboda kwayar cutar Lassa, “bera da yawa” ana samun su a duk fadin yankin.
Ta kara da cewa, an samu bullar cutar a kananan hukumomi 87 dake fadin jihohi 23 na tarayyar kasar nan.