Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ayyana cutar ƙyandar biri a matsayin matsala mai buƙatar kulawar gaggawa ta duniya.
Wannan ayyanawa ita ce matakin ankararwa mafi girma da WHO ta ɗauka sakamakon ƙaruwar masu kamuwa da cutar.
An bayyana matakin ne bayan kammala taron gaggawa da kwamati kan cutar ya gudanar a yau Asabar.
Mutum fiye da 16,000 ne ake zargin sun kamu da cutar a ƙasashe 75, a cewar shugaban WHO Dr Tedros Adhanom Ghebreyesus.
Ya ƙara da cewa ya zuwa yanzu cutar ta kashe mutum biyar.
Cutuka biyu ne kawai ke kan wannan matakin a yanzu. Su ne annobar korona da kuma yunƙurin da ake yi na kawar da cutar polio – wato shan-inna