fidelitybank

Cutar Kwalara ta kashe mutum bakwai a Kano

Date:

A jihar Kano, ana ci gaba da zaman makoki da alhinin rasuwar mutum bakwai waɗanda suka rasu a sakamakon cutar kwalara da suka kamu da ita bayan sun sha ruwan wata rijiya a wani ƙauye.

Bayanai na cewa lamarin ya auku ne sanadiyyar gurɓacewar ruwa sakamakon ambaliyar ruwa daga wani kudiddifi da ke kusa da rijiyar kuma kawo yanzu mutum fiye da 10 ne suke kwance a asibiti suna karɓar magani.

Bayanan daga ƙauyen Kanye da ke ƙaramar hukumar Kabo a jihar Kano na cewa mutanen garin sun fara ganin waɗanda suka harbu da cutar ta kwalara ne a unguwar da rijiyar take bayan da wasu magidanta suka yi amfani da ruwan rijiyar kuma suka kwanta rashin lafiya.

Kwamishinan lafiya na jihar ta Kano, Dokta Abubakar Labaran Yusuf ya ce ba shi da cikakken bayani tukuna, amma zai tura jami’ai don ƙara kai ɗauki da kuma bincike.

Sai dai bayanai na cewa a baya-bayan nan an samu mutuwar ɗimbin mutane a sassan jihar Kano sakamakon ɓullar cutar kwalara, inda hukumomi suka tabbatar da cewa cikin fiye da mutum 600 da ake fargabar sun kamu da cutar fiye da 30 ne suka mutu.

Ma’aikatar lafiya ta bayyana cewa ana kyautata zaton cewa ambaliyar ruwan da aka samu zuwa cikin wasu rijiyoyi ne ta haddasa kwalarar da ta yi sanadin mutuwar mutanen amma sun ce sun saka magani a wuraren.

daily post news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...
X whatsapp