fidelitybank

Cutar Kwalara ta kashe mutum bakwai a Kano

Date:

A jihar Kano, ana ci gaba da zaman makoki da alhinin rasuwar mutum bakwai waɗanda suka rasu a sakamakon cutar kwalara da suka kamu da ita bayan sun sha ruwan wata rijiya a wani ƙauye.

Bayanai na cewa lamarin ya auku ne sanadiyyar gurɓacewar ruwa sakamakon ambaliyar ruwa daga wani kudiddifi da ke kusa da rijiyar kuma kawo yanzu mutum fiye da 10 ne suke kwance a asibiti suna karɓar magani.

Bayanan daga ƙauyen Kanye da ke ƙaramar hukumar Kabo a jihar Kano na cewa mutanen garin sun fara ganin waɗanda suka harbu da cutar ta kwalara ne a unguwar da rijiyar take bayan da wasu magidanta suka yi amfani da ruwan rijiyar kuma suka kwanta rashin lafiya.

Kwamishinan lafiya na jihar ta Kano, Dokta Abubakar Labaran Yusuf ya ce ba shi da cikakken bayani tukuna, amma zai tura jami’ai don ƙara kai ɗauki da kuma bincike.

Sai dai bayanai na cewa a baya-bayan nan an samu mutuwar ɗimbin mutane a sassan jihar Kano sakamakon ɓullar cutar kwalara, inda hukumomi suka tabbatar da cewa cikin fiye da mutum 600 da ake fargabar sun kamu da cutar fiye da 30 ne suka mutu.

Ma’aikatar lafiya ta bayyana cewa ana kyautata zaton cewa ambaliyar ruwan da aka samu zuwa cikin wasu rijiyoyi ne ta haddasa kwalarar da ta yi sanadin mutuwar mutanen amma sun ce sun saka magani a wuraren.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp