Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce. a kowacce shakara akan samu kusan mutum miliyan 1.1 da ke kamuwa da cutar Kansa a nahiyar Afirka inda kusan mutum 700,000 ke mutuwa sakamakon cutar.
Daraktar hukumar mai lura da kasashen Afirka Dakta Matshidiso Moeti, ce ta bayyana haka ranar Lahadi a wani jawabi da ta gabatar a bikin ranar yaÆ™i da cutar ta duniya mai taken ‘Inganta Hanyoyin Yaki da Cutar: Mu haÉ—a muryoyinmu domin É—aukar mataki’.
Ta ce hasashen da aka yi yanzu na nuna cewa akwai barazanar samun kashi 50 cikin É—ari na yaran da ake haihuwa da cutar a nahiyar Afirka zuwa shekarar 2050.
Karanta Wannan:Â Za a gudanar da zabe lafiya a Zamfara – NSCDC
Ta ƙara da cewa alkaluman sun nuna cewa akwai hasashen samun ƙaruwar mace-mace sakamakon cutar kansa zuwa kusan miliyan ɗaya a kowacce shekara zuwa 2030, idan ba a ɗauki matakan da suka dace ba.
Dakta Moeti ta ce ƙasashe 12 ne a nahiyar Afirka ke da kyakkyawan shirin yaƙi da cutar.
Jami’ar ta WHO ta ce Hukumar na taimaka wa Æ™asashe 11 domin samar da ko inganta shirye-shiyensu na yaÆ™i da cutar.