fidelitybank

Cushe ya jawo cece-kuce tsakanin ministar kudi da ta jin kai

Date:

Batun nan na yi wa kasafin kudin 2023 na gwamnatin tarayya ciko da majalisar dattawa ke tuhumar ma’aikatar kudi ta kasar na ci gaba tayar da kura.

Kan wannan batun, Ministar jin kai ta aika wa takwararta ta ma’aikatar kudi wata wasika wadda a ciki ta dora alhakin bayyanar wasu naira biliyan 206 cikin kasafin kudin ma’aikatarta, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce tsakanin wadannan ma’aikatun gwamnatin biyu.

A makon jiya, yayin da ministar jin kai ta gwamnatin Najeriya ta halarci zaman majalisar dattawan kasar domin kare kasafin kudin ma’aikatarta, wani batu ya taso da ya janyo ce-ce-ku-ce.

Wani mamba na kwamitin ayyuka na musamman na majalaisar dattawan, Sanata Elisha Abbo, ya tambayi Minista Sadiya Farouk yadda – kamar yadda ya ce – yadda wasu bakin naira biliyan 206 suka bayyana cikin kasafin kudin ma’aikatar jin kai, wadda ke ƙarƙashin kulawarta.

Rahotanni a jaridun Najeriya sun ruwaito Minista Sadiya Farouk na dora alhakin bayyanar wadannan biliyoyin nairorin kan ma’aikatar kudi ta kasar.

Lamarin ya kai ga Minista Sadiya Farouk ta rubuta wata wasika kai tsaye ga takwararta, wato ministar kudi Zainab Ahmed, kuma a ciki ta nanata cewa ba ta hannu a wannan kutsen da kudaden suka yi wa kasafin kudin ma’aikatar tata, kuma ta dora laifin haka kan ministar.

To ma’aikatar kudi ta Najeriya ta fitar da wata sanarwa, wadda a ciki ta kare minista Zainab Ahmed daga tuhumar da minista Sadiya Farouk ta yi kan batun.

To idan akwai wani darasi da za a iya cewa na koya, shi ne har yanzu Najeriya ba ta iya kawar da batun nan na yi wa kasafin kudin kasar cuse ba, ta hanyar saka wasu kudade da tun farko ba a amince da su ba a hukumance.

Wani abin da ‘yan Najeriya kuma za su so gani shi ne ko wannan bayanin da ma’aikatar kudin Najeriya ta fitar zai gamsar da majalisar dattawar kasar, da kuma matakin da zai biyo baya.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...

Ambaliyar ruwa ta kashe mutuane takwas a Ebonyi

Ambaliya, wadda mamakon ruwan sama ya janyo, ta yi...

Bankin Duniya zai kashe wa yankin Arewa a Najeriya dala miliyan 300

Bankin Duniya ya amince da kasafin kuɗi dala miliyan...

Giyar mulki na kwasar Trump – ‘Yan Majalisar Democrat

'Yan Democrats a Amurka sun zargi Donald Trump da...

Kama Aminu Waziri Tambuwal da EFCC ta yi ba daidai ba ne – PDP

Jam'iyyar PDP a jihar Sokoto ta yi Allah-wadai da...

An kai hari a ƙauyuka 15 na Zamfara a mako ɗaya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...
X whatsapp