fidelitybank

Covid-19: Da yiwuwar adadin talakawa su karu a shekarar 2022

Date:

Gwamnatin Tarayya ta ce akwai yiwuwar yawan talakawa su karu zuwa miliyan 109 nan da karshen shekarar 2022.

Ministar Kudi, Kasafi da tsare-tsare, Zainab Ahmed ce ta bayyana hakan, ta ce sabbin mutum miliyan 11 na iya fada wa kangin talauci a cikin shekarar, sakamakon annobar COVID-19.

Zainab Ahmed ta furta hakan ne a Abuja ranar Talata, a ci gaba da taron da ake yi kan annobar COVID-19 mai taken ‘Fadan karshe wajen yaki, tare da murmurewa daga annobar COVID-19’.

Ministar, wacce ta sami wakilcin Darakta Janar na Ofishin Kasafin Kudi, Ben Akabueze, ta ce”Akalla mutum miliyan biyu ne suka fada talauci a 2020, saboda yadda yawan jama’a ya zarce karfin tattalin arzikin kasa, annobar ta COVID-19 da kuma karyewar tattalin arziki sun kara yawan wasu matalautan da kimanin miliyan 6.6, lamarin da ya kawo adadin zuwa miliyan 8.6 a cikin shekarar kawai. Hakan na nuni da yiwuwar karuwar talakawa a Najeriya daga miliyan 90 a 2020 zuwa miliyan 109 a 2022”. A cewar Zainab.

Jaridar Aminiya ta alakanta kalubalen da yawan karuwar ayyukan da ba su da tabbas, wadanda ta ce su ma sun dada jefa jama’a cikin kangin talaucin.

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp