Gwamnatin Tarayya ta ce akwai yiwuwar yawan talakawa su karu zuwa miliyan 109 nan da karshen shekarar 2022.
Ministar Kudi, Kasafi da tsare-tsare, Zainab Ahmed ce ta bayyana hakan, ta ce sabbin mutum miliyan 11 na iya fada wa kangin talauci a cikin shekarar, sakamakon annobar COVID-19.
Zainab Ahmed ta furta hakan ne a Abuja ranar Talata, a ci gaba da taron da ake yi kan annobar COVID-19 mai taken ‘Fadan karshe wajen yaki, tare da murmurewa daga annobar COVID-19’.
Ministar, wacce ta sami wakilcin Darakta Janar na Ofishin Kasafin Kudi, Ben Akabueze, ta ce”Akalla mutum miliyan biyu ne suka fada talauci a 2020, saboda yadda yawan jama’a ya zarce karfin tattalin arzikin kasa, annobar ta COVID-19 da kuma karyewar tattalin arziki sun kara yawan wasu matalautan da kimanin miliyan 6.6, lamarin da ya kawo adadin zuwa miliyan 8.6 a cikin shekarar kawai. Hakan na nuni da yiwuwar karuwar talakawa a Najeriya daga miliyan 90 a 2020 zuwa miliyan 109 a 2022”. A cewar Zainab.
Jaridar Aminiya ta alakanta kalubalen da yawan karuwar ayyukan da ba su da tabbas, wadanda ta ce su ma sun dada jefa jama’a cikin kangin talaucin.