Ministan Abuja, Nyesom Wike ya goyi bayan ayyana dokar ta-ɓaci da shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yi a jihar Rivers.
Da yake jawabi ga wasu manema labari a birnin Abuja, tsohon gwamnan na jihar Rivers ya ce so ya yi a cire gwamnan jihar Siminalayi Fubara ba dakatarwa ba.
A wani mataki da ke ci gaba da raba kan ƴan ƙasar, shugaba Tinubu ya dakatar da gwamnan Fubara tare da mataimakiyarsa, Ngozi Odu da mambobin majalisar dokokin jihar, bayan kwashe watanni ana dambarwar siyasa a jihar.
Wike ya ce matakin shugaban ƙasar ya ceto jihar daga faɗawa rikici, yana mai cewa naɗa kantoman riƙo a jihar kyakkyawan mataki ne.