Cibiyar bunkasa fasahar sadarwa da ci gaban al’umma, CITAD, ta yi kira ga gwamnatoci da al’umma da su tashi tsaye, domin ganin an kawo karshen cin zarafin ‘ya’ya mata da a ke yi a kasar nan.
CITAD ta yi wannan kira ne yayin taron manema labarai, ta ce dole ne al’umma su tashi tsaye, domin ganin sun kawo karshen cin zarafin ‘ya’ya mata da kana nan yara.
Jami’ar kula da jinsi ta cibiyar, Zainab Aminu, ta ce” A watan Nuwamban da ya gabata mun samu korafe-korafe guda 22 ta manhajar tura korafi da cibiyar ta samar, wadanda mu ka hada da na fyade da cin zarafi daban-daban da al’umma su ke fama dasu”.
Cibiyar ta CITAD ta kuma ce, rahoton da suka samu daga wajen, hukumar kare hakkin dan Adam ta kasa, ya bayyana cewa, an samu rahoton cin zarafin yara kanana guda 50, sannan an samu rahoton cin zarafin mata guda 75