fidelitybank

Cin zarafin Daliba ya sanya yin zanga-zanga a China

Date:

Zanga-zanga ta ɓarke a kudancin China sakamakon cin zarafin wata ɗaliba ƴar shekara 14 inda mutane ke ta neman a yi mata adalci.

A makon da ya gabata ne wani bidiyo da a ciki wasu sa’annin yarinyar suke zabga mata mari da kuma tilasta mata tsayawa kan gwiwoyinta ya karaɗe shafukan sada zumunta a birnin Jiangyou da ke Lardin Sichuan.

Ƴansanda sun ce yaran da ake zargi da cin zarafin ɗalibar – dukkansu mata ne ƴan shekara 13 da 14 da kuma 15, kuma an tura biyu daga cikinsu makarantu na musamman domin gyara masu tarbiyya.

Bayan da labarin yarinyar ya bazu a shafukan sada zumunta, wasu da dama na ganin an yi sassauci a matakin da aka ɗauka kan waɗanda ake zargi – musamman bayan iƙirarin da ke nuna cewa an ɗaɗe ana cin zarafin yarinyar kuma mahaifiyarta, wadda kurma ce, ta roƙi hukumomi su yi wa ɗiyarta adalci.

Lamarin dai ya fusata mutane da dama har ma zanga-zanga ta ɓarke a wajen ofisoshin ƙaramar hukumar dake Jiangyou.

Fiye da mutum 1,000 ne suka taru kan titi jiya Litinin inda suka kai har tsakaddare a wajen, kamar yadda masu shaguna da ke wurin suka bayyana.

Ɗaya daga cikinsu ya shaida wa BBC cewa “lamarin ya ƙazanta” bayan da ƴansanda suka tarwatsa mutanen da suka taru.

bbc news nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp