fidelitybank

Cin zarafi a Kano ya karu – Hukumar Kare Hakkin Dan Adam

Date:

Hukumar kare hakkin dan adam a jihar Kano, ta ce, a shekarar da ta gabata sun karbi korafe-korafen tauye hakkin dan adam har dubu daya da dari biyar daga sassan jihar.

Shugaban hukumar ya shaida wa BBC cewa, akasarin korafe-korafe sun shafi cin zarafin kananan yara da kuma fyade, sai batun zamantakewar aure inda suka samu nasarar shawo kan matsaloli fiye da dubu daya.

Hukumar kare hakkin dan adam din reshen jihar Kano ta ce daga watan Janairu zuwa watan Disambar bara sun karbi korafe-korafen take hakkin bani-adama har dubu daya da dari biyar, wadanda suka shafi zamantakewa ta iyali.

Sai dai kuma hukumar ta ce akwai wasu matsalolin da suka shafi cin zarafin mata da kananan yara, kamar yada Shehu Abdullahi babban jami’in a hukumar ya shaidawa BBC.

Shehu Abdullahi ya ce cikin korafe-korafen dubu daya da dari biyar, sun yi aiki walau na shari’a ko na zama tare da tattaunawa da wadanda abin ya shafa har dubu daya da dari biyu da casa’in da shida.

Kana matsaloli fiye da dari biyu ana ci gaba da aiki akansu.

Jami’in ya kuma ce akwai bukatar samar da kyakkyawan yanayi na aikin yi da walwalar tattalin arziki tsakanin al’umma, musamman mata ta hanyar samar musu da ayyukan yi a gidanjensu.

Bayanai na cewa a baya, ‘yan uwa da dangi da kuma abokan arziki kan warware tare da sasanta duk wani korafi ko rikici, amma a yanzu hakan ya yi karanci, al’amarin da yasa ake tururuwar kai korafe-korafe zuwa hukumar kare hakkin dan adam.

sunnnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar Æ´ansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na É—aya daga cikin jhihohin da ake kaÉ—a...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...
X whatsapp