fidelitybank

Cin zalin yara ba shi da gurbi a kasar mu – Tinubu

Date:

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cin zalin yara a matsayin abin Allah-wadai da ya ce ba za a lamunta da ci gaba da shi ba a Najeriya.

Tinubu ya sanar da hakan a cikin wani bayani da aka fitar a yau Talata albarkacin Ranar Yara ta ta duniya bana.

“Al’ummar da yara ke samun kulawa da natsuwa, ake martaba su tare da sauraren su a sarari da kuma sauran ɓangarori a cikin, ita ce mai samun cigaba a duniya. A zahiri ya ke cin fuskar yara da walaƙanta su ba shi da muhalli a Najeriya,” in ji shugaba Tinubu.

Shugaban Najeriyar ya ce ƙasarsa na cikin na gaba-gaba da ake cin zarafin yara a makarantu da sauran wurare, “A duniya, yaro ɗaya a cikin uku na fuskantar cin zali. Bincike ya nuna a Najeriya yawan samun cin zalin yara ‘yan shekarun zuwa makaranta ya kai kashi 65 cikin ɗari, waɗanda ke fuskantar hakan a zahiri da kuma ke da illa ga tunani ko alaƙarsu da sauran jama’a. Duk yaron da ke koyo cikin halin tsoro ba zai taɓa gane kome ba,” in ji Tinubu.

Shugaban Najeriyar ya ce gwamnatin tarayyar ƙasar da jahohi na ɗaukar matakan da suka dace domin kare yara daga fuskantar cin zarafi, waɗanda ya bayyana da “manyan gobe kuma ƙashin bayan ci gaban ƙasa”.

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp