Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cin zalin yara a matsayin abin Allah-wadai da ya ce ba za a lamunta da ci gaba da shi ba a Najeriya.
Tinubu ya sanar da hakan a cikin wani bayani da aka fitar a yau Talata albarkacin Ranar Yara ta ta duniya bana.
“Al’ummar da yara ke samun kulawa da natsuwa, ake martaba su tare da sauraren su a sarari da kuma sauran ɓangarori a cikin, ita ce mai samun cigaba a duniya. A zahiri ya ke cin fuskar yara da walaƙanta su ba shi da muhalli a Najeriya,” in ji shugaba Tinubu.
Shugaban Najeriyar ya ce ƙasarsa na cikin na gaba-gaba da ake cin zarafin yara a makarantu da sauran wurare, “A duniya, yaro ɗaya a cikin uku na fuskantar cin zali. Bincike ya nuna a Najeriya yawan samun cin zalin yara ‘yan shekarun zuwa makaranta ya kai kashi 65 cikin ɗari, waɗanda ke fuskantar hakan a zahiri da kuma ke da illa ga tunani ko alaƙarsu da sauran jama’a. Duk yaron da ke koyo cikin halin tsoro ba zai taɓa gane kome ba,” in ji Tinubu.
Shugaban Najeriyar ya ce gwamnatin tarayyar ƙasar da jahohi na ɗaukar matakan da suka dace domin kare yara daga fuskantar cin zarafi, waɗanda ya bayyana da “manyan gobe kuma ƙashin bayan ci gaban ƙasa”.