fidelitybank

Cin zaben da NNPP ta yi a Kano cuwa-cuwa ne – Ata

Date:

Ministan Jiha na Gidaje da Cigaban Birane, Rt Hon Yusuf Abdullahi Ata, ya yi kira ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) da ta soke zaɓen cike gurbi na majalisar dokokin jihar Kano da aka gudanar a mazabar Bagwai/Shanono, inda ya bayyana shi a matsayin cuwa-cuwar siyasa.

Ata, wanda ya yi jawabi ga manema labarai a Kano a ranar Lahadi, ya ce jam’iyyun siyasa sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya kafin zaɓen, amma jam’iyyar NNPP ta karya yarjejeniyar ta hanyar shigo da matasa dauke da makamai daga makwabtan Jihohi. Ya ce hakan ya kai ga kai hari ga magoya baya da kuma gidan ɗan takarar APC.

Ya bayyana cewa a ranar zaɓe an shigo da dubban ’yan daba dauke da makamai tun da asubahi, lamarin da ya tilasta jama’a gudu daga kauyuka. A cewarsa, ’yan daba sun kwace kayan zaɓe da suka haɗa da takardun zaɓe da sakamakon sannan suka cika su da dangwalawa ƙuri’un jam’iyyar NNPP.

Ministan ya ce al’ummar mazabar da suka shafe sama da shekara guda suna jiran gudanar da zaɓen sun kasance cikin takaici da rashin adalci. Ya roƙi magoya baya da su kwantar da hankulansu tare da kira ga hukumomin tsaro da su gurfanar da duk wasu da aka kama.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Cin zaben da NNPP ta yi a Kano cuwa-cuwa ne – Ata

Ministan Jiha na Gidaje da Cigaban Birane, Rt Hon...

Mutane kusan 40 sun ɓace sakamakon haɗarin kwale-kwale a Sokoto

Aƙalla mutum 40 ne ake nema bayan haɗarin kwale-kwale...

APC ta yi kwaf daya a zaben cike gurbin Kaduna da Jigawa

Jam'iyyar APC mai mulki a jihar Jigawa ta yi...

Ba mu yarda da zaben Ghari da Tsanyawa ba – NNPP

Jam'iyar NNPP mai mulkin jihar Kano a arewacin Najeriya...

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...
X whatsapp