fidelitybank

Cin zaben da NNPP ta yi a Kano cuwa-cuwa ne – Ata

Date:

Ministan Jiha na Gidaje da Cigaban Birane, Rt Hon Yusuf Abdullahi Ata, ya yi kira ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) da ta soke zaɓen cike gurbi na majalisar dokokin jihar Kano da aka gudanar a mazabar Bagwai/Shanono, inda ya bayyana shi a matsayin cuwa-cuwar siyasa.

Ata, wanda ya yi jawabi ga manema labarai a Kano a ranar Lahadi, ya ce jam’iyyun siyasa sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya kafin zaɓen, amma jam’iyyar NNPP ta karya yarjejeniyar ta hanyar shigo da matasa dauke da makamai daga makwabtan Jihohi. Ya ce hakan ya kai ga kai hari ga magoya baya da kuma gidan ɗan takarar APC.

Ya bayyana cewa a ranar zaɓe an shigo da dubban ’yan daba dauke da makamai tun da asubahi, lamarin da ya tilasta jama’a gudu daga kauyuka. A cewarsa, ’yan daba sun kwace kayan zaɓe da suka haɗa da takardun zaɓe da sakamakon sannan suka cika su da dangwalawa ƙuri’un jam’iyyar NNPP.

Ministan ya ce al’ummar mazabar da suka shafe sama da shekara guda suna jiran gudanar da zaɓen sun kasance cikin takaici da rashin adalci. Ya roƙi magoya baya da su kwantar da hankulansu tare da kira ga hukumomin tsaro da su gurfanar da duk wasu da aka kama.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp