fidelitybank

Cin Amana: Matashi ya kashe abokin sa ya gudu da motarsa da Naira miliyan 2 zuwa Kano

Date:

Man in cuffs

Bashir ne babban abokin mamacin yayin da ya yi aure ‘yan watannin da suka gabata.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa, Bashir ya gayyaci mamacin ne mai shekara 28 da haihuwa zuwa unguwar Tudun Fulani ta birnin Minna kimanin mako biyu da ya gabata domin su tattauna kan wata damar kasuwanci da ta bayyana a cewarsa.

Sai dai Bashir ya daba wa amamacin wuka bayan da ya isa wurin, kuma ya tsere da motarsa kirar Peugeot 206 da kuma Naira miliyan biyu da ke cikin motar.

Rundunar ‘yan sandan Najeriya da ke jihar ta Neja ta tabbatar da aukuwar lamarin ta hannun kakakinta DSP Wasiu Abiodu, wanda yace bincike ya sa sun kama Bashir da wani wanda ya taimaka masa mai suna Aliyu Ibrahim wanda ke da shekara 22 da haihuwa.

Akwai kuma wani Suleiman Mahmud da shi ma ake tuhuma da hannu wajen aikata wannan aika-aikar, wanda tuni ya tsere, sai dai ‘yan sanda na ci gaba da nemansa.

Jaridar ta kuma ce Bashir ya tsere da motar ne zuwa Kano, domin ya sayo wasu sinadarai da ake wanke zinare da su da kudin mamacin.

Sai dai bayan ya koma Minna ne ‘yan sanda suka damke shi a wani otel da ke kan babbar hanyar Wetern Bypass a Minna.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp