Wani dan acaba ya fada komar ‘yan sandan jihar Abia, bayan da ake tuhumar sa da laifin kashe abokin sana’arsa wani wurin siyar da abinci.
Jaridar The Nation ta rawaito cewa, lamarin ya auku ne a layin Uzompka da ke unguwar Amaiyi a yankin Owerri-Aba a cikin karamar hukumar Ugwunagbo ranar Litinin.
Wani ganau ya shaida cewa, mutumin ya je siyan abinci inda ya bukaci mai sayar da abinci ta dakata da zuba wa kowa sai shi kawai a nan ne suka fara kace nace ta kai ga an rasa rai.
Mamacin bai dade da shiga wurin cin abinci ba, wanda aka sa wa suna Nwanyi Mmonghon tare da wani Chinenye wanda ake zargi.