fidelitybank

Cikin watanni 14 za a kammala Titin Abuja zuwa Kaduna da Kano – Gwamnati

Date:

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya sake ƙaddamar da aikin sabunta titin Abuja-Kaduna-Kano.

Da yake jawabi a madadin shugaban a wajen ƙaddamar, gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya bayyana titin a matsayin mai muhimmanci, wanda ya ce yana haɗa babban birnin tarayyar ƙasar da sama da jihohi 12 a arewa maso yamma da arewa ta tsakiya da arewa ta gabashin ƙasar.

A wajen taron wanda aka yi a garin Jere da ke ƙaramar hukumar Kagarko, Uba Sani ya ce an yi watsi da hanyar na tsawon lokaci, wanda hakan a cewarsa ya jawo asarar rayuka da illata tattalin arzikin ƙasar.

“Sabunta wannan titin zai sauƙaƙa zirga-zirga, sannan zai samar da ayyukan yi tare da inganta tsaro da walwalar al’umma,” in ji shi kamar yadda ya bayyana a shafinsa na Facebook.

Ya ce abin da ya jawo tsaikon aikin a baya shi ne rashin tsaro, wanda ya ce yanzu ana samu nasara a ɓangaren, inda ya ce matafiya suna tafiya a kowane lokaci ba tare da fargaba ba.

A nasa ɓangaren, ministan ayyuka, David Umahi ya yaba da ƙoƙarin gwamnatin jihar Kaduna wajen tabbatar da an ci gaba da aikin, inda ya tabbatar da cewa za a kammala aikin a cikin wata 14.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp