fidelitybank

Cikin watanni 14 za a kammala Titin Abuja zuwa Kaduna da Kano – Gwamnati

Date:

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya sake ƙaddamar da aikin sabunta titin Abuja-Kaduna-Kano.

Da yake jawabi a madadin shugaban a wajen ƙaddamar, gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya bayyana titin a matsayin mai muhimmanci, wanda ya ce yana haɗa babban birnin tarayyar ƙasar da sama da jihohi 12 a arewa maso yamma da arewa ta tsakiya da arewa ta gabashin ƙasar.

A wajen taron wanda aka yi a garin Jere da ke ƙaramar hukumar Kagarko, Uba Sani ya ce an yi watsi da hanyar na tsawon lokaci, wanda hakan a cewarsa ya jawo asarar rayuka da illata tattalin arzikin ƙasar.

“Sabunta wannan titin zai sauƙaƙa zirga-zirga, sannan zai samar da ayyukan yi tare da inganta tsaro da walwalar al’umma,” in ji shi kamar yadda ya bayyana a shafinsa na Facebook.

Ya ce abin da ya jawo tsaikon aikin a baya shi ne rashin tsaro, wanda ya ce yanzu ana samu nasara a ɓangaren, inda ya ce matafiya suna tafiya a kowane lokaci ba tare da fargaba ba.

A nasa ɓangaren, ministan ayyuka, David Umahi ya yaba da ƙoƙarin gwamnatin jihar Kaduna wajen tabbatar da an ci gaba da aikin, inda ya tabbatar da cewa za a kammala aikin a cikin wata 14.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp