Hukumomin Sudan ta Kudu sun ce, an hallaka mutum sama da mutum 230 a cikin mako biyu a rikici kan shanu da wurin kiwo a kudancin kasar.
Fadan ya barke ne tun daga farkon watan nan a yankin Kapoeta inda kabilu da ke gaba da juna ke ta tafka rikici.
Wadanda aka kashe sun hada da wani basaraken yankin wanda aka harba yayin da ake jana’izar wasu da aka kashe a rikicin.
Gwamnan jihar da ake rikicin ya soki lamarin tare da yin kira ga gwamnati da ta hanzarta tura jami’an tsaro domin kwantar da hankali.
Fadan ya barke ne yayin da kasar ke cika shekara 11 da samun ‘yanci daga Sudan. In ji BBC.
Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa, kasar na cikin hadarin sake fadawa yakin basasa saboda rikicin kabilanci, wanda tuni ya raba miliyoyin mutane da gidajensu.