fidelitybank

Cigaba da dogara a kan man fetur kaɗai zai ƙara jefa Najeriya cikin talauci da rashin aikin yi – Tajudeen Abbas

Date:

Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ya yi gargadin cewa ci gaba da dogaro da man fetur kadai zai kara talauci, da rashin aikin yi a Najeriya.

Abbas ya bayyana hakan ne yayin da yake gabatar da jawabi a wajen taron karramawar digiri karo na 14 na Jami’ar Al-Hikmah da ke Ilorin, ranar Litinin.

Ya ce lokaci ya yi da Najeriya za ta fara amfani da dimbin albarkatun da take da su tare da karfin dan Adam domin fadada tattalin arzikinta.

Ya kara da cewa, don tabbatar da makomar tattalin arzikin kasar, dole Najeriya ta daina dogaro da mai kawai ta kuma bullo da sabbin hanyoyin bunkasa ci gaba mai dorewa.

Ya ce, “Tare da raguwar kudaden shiga daga man fetur, sauyin yanayin duniya zuwa makamashi mai sabuntawa, da kuma bukatar samar da ayyukan yi, dole mu yi gaggawar tsara sabon tsari don sauya tattalin arzikinmu.

“Wannan yana bukatar kokari na musamman don bude damammakin wasu bangarori, kamar noma, ma’adanai, fasaha da masana’antar kere-kere.

“Samun wannan sauyin zai tabbatar da makomar tattalin arzikin Najeriya, tare da magance matsalolin talauci, da rashin aikin yi, wanda su ne manyan kalubale ga ci gaba mai dorewa,” in ji shi.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp