fidelitybank

Cigaba da dogara a kan man fetur kaɗai zai ƙara jefa Najeriya cikin talauci da rashin aikin yi – Tajudeen Abbas

Date:

Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ya yi gargadin cewa ci gaba da dogaro da man fetur kadai zai kara talauci, da rashin aikin yi a Najeriya.

Abbas ya bayyana hakan ne yayin da yake gabatar da jawabi a wajen taron karramawar digiri karo na 14 na Jami’ar Al-Hikmah da ke Ilorin, ranar Litinin.

Ya ce lokaci ya yi da Najeriya za ta fara amfani da dimbin albarkatun da take da su tare da karfin dan Adam domin fadada tattalin arzikinta.

Ya kara da cewa, don tabbatar da makomar tattalin arzikin kasar, dole Najeriya ta daina dogaro da mai kawai ta kuma bullo da sabbin hanyoyin bunkasa ci gaba mai dorewa.

Ya ce, “Tare da raguwar kudaden shiga daga man fetur, sauyin yanayin duniya zuwa makamashi mai sabuntawa, da kuma bukatar samar da ayyukan yi, dole mu yi gaggawar tsara sabon tsari don sauya tattalin arzikinmu.

“Wannan yana bukatar kokari na musamman don bude damammakin wasu bangarori, kamar noma, ma’adanai, fasaha da masana’antar kere-kere.

“Samun wannan sauyin zai tabbatar da makomar tattalin arzikin Najeriya, tare da magance matsalolin talauci, da rashin aikin yi, wanda su ne manyan kalubale ga ci gaba mai dorewa,” in ji shi.

the nation newspaper nigeria today latest

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp