fidelitybank

Chukwueze ya kafawa Real Madrid tarihi har gidan ta

Date:

Samuel Chukwueze shi ne tauraron ɗan wasa, yayin da Villarreal ta samu nasarar doke zakarun gasar, Real Madrid da ci 3-2 a gasar La Liga da suka fafata a ranar Asabar.

Mintuna 16 da fara wasan a Santiago Bernabeu, ƙungiyar ta Yellow Submarine ta samu kanta a baya, bayan da mai tsaron baya Pau Torres ya ci gida.

Chukwueze ne ya dawo da martabar maziyartan a lokacin da ya wuce Nacho Fernandez, inda ya ci kwallonsa ta farko a minti na 39 da fara wasa.

Karanta Wannan: Messi ya zarce Ronaldo a cin ƙwallaye

Dan wasan Brazil Vinicius Junior ne ya sake jefa kwallo a ragar Los Blancos bayan mintuna bakwai.

Jose Morales wanda ya maye gurbinsa ya ramawa Villarreal a minti na 70. Daga nan sai Chukwueze ya farke kwallon da ta yi nasara a minti na 80 daga dogon zango, inda ya kai Real Madrid rashin nasararta ta farko a gida a gasar cikin gida a bana.

Da rawar da ya taka, Samuel Chukwueze ya zama dan wasan Villarreal na biyu da ya ci kwallaye biyu a gasar La Liga a Santiago Bernabeu da Real Madrid, bayan Diego Forlan a watan Mayun 2006.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp