China za ta daina killace matafiya daga ranar 8 ga watan Janairu lamarin da zai kawo gagarumin sauyi kan matakinta na yaki da annobar korona, a cewar jami’ain gwamnatin kasar.
Bayan ta shafe kusan shekaru uku iyakokinta a kulle, yanzu za a bai wa masu bisar aiki da karatu da kuma wadanda ke son ziyartar iyalansu damar shiga kasar.
Wannan sauyi na zuwa ne a daidai lokacin da China take fama da karin yaduwar cutar korona bayan ta janye takunkumin da ta sanya wa ‘yan kasar na kulle.
Rahotanni sun ce asibitoci sun cika makil da marasa lafiya kuma tsofaffi na ta mutuwa.
A halin yanzu ba a san adadin mutanen da ke mutuwa sanadin cutar a kullum ba saboda an daina sanar da alkaluman wadanda suke mutuwa.
A makon jiya Beijing ta bayar da rahoton cewa kusan mutum 4,000 ke kamuwa da cutar Covid a kullum kuma ana samun mutuwa nan da can.