Ofishin jakadancin kasar China a Najeriya ya karyata labarin da ke cewa, jamhuriyar jama’ar kasar Sin na goyon bayan aniyar shugaban kasa na ministan sufurin Najeriya Rotimi Chibuike Amaechi.
A cikin wata sanarwar manema labarai da ofishin jakadancin ta fitar, China ta bayyana jita-jitar a matsayin “labaran karya, wanda aka kirkira da wasu dalilai na boye.”
Sanarwar ta kara da cewa, “An jawo hankalin ofishin jakadancin kasar Sin kan wani rahoto na batanci kan wata kafar yada labarai ta internet, inda ake zargin Mista Rotimi Amaechi, ministan sufurin Najeriya kuma daya daga cikin masu neman tsayawa takarar shugabancin kasar a 2023. , ya samu goyon bayan gwamnatin kasar Sin, kuma an gudanar da tarurruka da dama tsakanin abokan Amaechi da gwamnatin kasar Sin’, har ma da ikirarin cewa “China na bukatar … dora ikonta a Afirka”.
“Ana kara tunatar da jama’a da su yi watsi da shi, su kuma sanya ido kan irin wannan labaran na bogi, wadanda aka kirkira da wasu munanan dalilai. Girmama juna da rashin tsoma baki a cikin harkokin cikin gidan juna, shi ne babban ka’ida da kuma dogon lokaci na diflomasiyyar kasar Sin.