fidelitybank

Chelsea ta dauki dan wasan Ivory Coast

Date:

Ƙungiyar kwallon ƙafa ta Chelsea ta kammala ɗaukar ɗan wasan gaba na Ivory Coast David Datro Fofana daga ƙungiyar Molde da ke Norway a kan kuɗin fam miliyan takwas zuwa 10.

Ɗan wasan mai shekara 20 – wanda kuma ya ci kwallo 24 a wasa 65 da ya buga wa Molde – ya saka hannu kan kwantiragin shekara shida da ƙungiyar ta stamford bridge zuwa shekarar 2029, tare da zaɓin tsawaita kwantiragin.

Shi ne ɗan wasa na biyu da ƙungiyar ta saya cikin wannan wata na Janairu bayan ɗan wasan bayan Faransa Benoit Badiashile da ta saya daga Monaco kan fam miliyan 35.

“Ina cike da farin cikin zuwa ƙungiyar da na daɗe ina mafarkinta” in ji Fofana.

Chelsea ta bayyana ɗan wasan da cewa ”mai hazaƙar zura in ƙwallaye, kuma ɗaya daga cikin matasan ‘yan ƙwallon da suke da makoma mai kyau a nan gaba”.

Haka kuma ƙungiyar na kan tattaunawa da da Benfica kan ɗaukar matashin ɗan wasan tsakiyar Argentina Enzo Fernandez mai shekara 21, wanda ƙa’idar da ke cikin yarjejeniyar cinikinsa ta kai fam miliyan 106.

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ƴan Bindiga – Ɗan majalisa

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...
X whatsapp