Hukumomin Chadi sun sanar cewa, ƙasar za ta bude ofishin jakadancinta a Isra’ila ranar Alhamis bayan da kasashen biyu suka sabunta dangantakar diflomasiyya a 2019.
Shugaba Mahamat Deby ya gana da firaminista Benjamin Netanyahu yayin wata ziyarra aiki da ya kai Isra’ila a ranar Laraba.
Chadi kasa ce da yawancin al’ummarta Musulmi ne, ta yanke huldar diflomasiyya da Isra’ila a 1972.
Karanta Wannan: Sojoji sun kashe ‘yan tayar da kayar baya a Tafkin Chadi
Ofishin Mista Netanyahu ya sanar cewa shugabannin biyu za su halarci bikin bude ofishin jakadancin, sai dai bai bayyana wurin da aka ajiye shi ba. Yawancin kasashe na da ofisoshinsu na jakadanci a birnin Tel Aviv ne.
A ‘yan shekarun nan, Isra’ila na wani yunkurin bunkasa dangantakar diflomasiyya da kasashen Afirka masu yawa.