Ƙasar Chadi ta rufe kan iyakarka ta gabashi da ƙasar Sudan.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ce ƙasar ta rufe kan iyakar ne har zuwa wani lokaci da ba a bayyana ba.
A wata sanarwa da gwamnatin Chadin ta fitar, ta ce tana kira ga ƙasashen Afirka da na duniya da ƙasashen makwabta da su taimaka wajen maido da zaman lafiya a Sudan.


