fidelitybank

Chadi ta janye Jakadanta daga Isra’ila

Date:

Ƙasar Chadi ta ce ta kira jakadanta a Isra’ila zuwa gida don tattaunawa game da “hare-hare da tashin hankalin da ba a taɓa gani ba a Zirin Gaza”.

Cikin wata sanarwa daga ma’aikatar harkokin wajen ƙasar, gwamnati ta yi tir da “rasa rayukan fararen hula kuma ta yi kira a tsagaita wutar da za ta kai ga samun kwanciyar hankali ga Falasɗinawa”.

A shekarar 1972, Chadi wadda Musulmai suka fi rinjaye, ta yanke hulɗar da jakadanci tsakaninta da Isra’ila, har sai a 2019 suka daidaita.

Yanzu Chadi ta zama ƙasar Afirka ta farko da ta ɗauki irin wannan mataki tun bayan fara yaƙin a ranar 7 ga watan Oktoba.

Zuwa yanzu, ƙasashen Turkiyya, da Chile, da Bahrain, da Honduras, da Colombia, da Jordan sun janye jakadunsu daga Isra’ila don nuna ɓacin ransu da hare-haren na Isra’ila a Gaza.

Isra’ila ta ce mayaƙan Hamas sun kashe mutum 1,400 lokacin da suka kai hari ranar 7 ga Oktoba, inda ta ci alwashin ganin bayan ƙungiyar a hare-haren ramuwar gayya – waɗanda suka kashe Falasɗinawa sama da 9,500 zuwa yanzu.

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp