fidelitybank

CBN zai fara cire kuɗi a asusun mutane

Date:

Babban bankin kasa CBN, ya bai wa bankuna a ƙasar umarni da su fara cire kashi 0.5 cikin 100 a duk lokacin da aka tura kuɗi ta asusun banki a matrsayin kuɗaɗen tabbatar da tsaro ta intanet.

Cikin wata sanarwa ɗauke da sa hannun Chibuzor Efobi, Daraktan kula da tsarin biyan kuɗi da Haruna Mustafa, Daraktan kula da manufofin kuɗi, babban bankin ya ce za a fara aiwatar da wannan tsari ne nan da makonni biyu masu zuwa.

A cewar CBN, kuɗin da za a cira domin tara harajin tsaron intanet ya zo ne sakamakon amincewa da dokar yaƙi da laifukan intanet ta 2024 da aka yi wa gyaran fuska.

Sanarwar ta ce za a zuba kuɗin da aka cira ne a asusun tsaron intanet na ƙasa wanda zai kasance a ƙarƙashin ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro.

Tsarin bai shafi masu karɓa da biyan bashi ba da kuɗaɗen albashi da kuma mutumin da zai tura kuɗi daga asusun ajiyarsa na banki zuwa wani asusun nasa na daban da kuma masu tura kuɗi zuwa wani asusun na banki ɗaya.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp