Majalisar Dattaijai ta umarci Babban Bankin CBN da ya sake duba matsayarsa na takaita cirar kudi daga bankuna saboda yadda jama’ar kasar ke kokawa kan sabon tsarin.
Majalisar Dattijan ta bayyana haka ne bayan doguwar mahawara tsakanin ‘yan majalisar a jiya Laraba.
Majalisar ta umarci kwamitin da ke kula da harkokin bankuna da kudade da ya je ziyarar duba ayyukan CBN yayin da yake aiwatar da sabon tsarin kuma ya bai wa majalisar rahotonsa na lokaci zuwa lokaci.
Wasu daga cikin ‘yan majalisar sun kalubalanci sabon tsarin na CBN na rashin tuntuba kan manufar, kafin aiwatar da shi.
Kazalika, wasu daga cikinsu ke cewa tsarin zai sa masu sana’ar cirar kudi na POS rasa ayyukansu.