fidelitybank

CBN ya rarrashi al’umma a kan rikicin dala da Naira

Date:

Babban bankin ƙasa CBN, ya kwantar da hankula mutane kan fargabar da ake nunawa na karuwar farashin dala da ke sake durkusar da Naira, yana cewa, zai yi kokari domin ganin an samu sassauci.

Wannan na zuwa ne bayan bankin ya gargadi masu yaɗa jita-jita a kasuwanni bayan fagge.

A lokacin da ya ke tsokaci kan karuwar farashin dala wanda tuni ake ganin tasirin haka a wajen ciniki da sauran kasuwanci, Daraktan harkokin yada labarai, Mista Osita Nwanisobi, ya ce, bankin ya durƙufa wajen ganin ya shawo kan manyan ƙalubalen da kasuwar canji ke fuskanta, da kuma ganin an kawo sauki.

CBN ya ce, babu shaka ana fama da ƙarancin dala musamman a wannan lokaci da bukatar dalar ke karuwa ga manya kamfanoni da masu biyan kudin makaranta da kiwon lafiya da dai saransu.

Sai dai ya ce, bankin a yanzu damuwarsa shi ne darajar Naira, da kuma ganin yada za a taimaki Najeriya wajen daidaita kuɗinta da kuma matsalolin da ake samu ta fanin cinikin mai.

A makon da ya gabata sai dai kungiyar masu canjin kudin kasashen waje ta yi kira ga gwamnatin kasar da ta dauki matakan dakatar da faduwar da darajar takardar kudin kasar ke cigaba da yi a kan dalar Amurka.

Kungiyar ta ce a cikin makon farashin dalar ya karu da kusan Naira 100, abin da ba a taba gani ba a tarihi

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp