fidelitybank

CBN ya musanta rahoton rashin isassun takardun buga kudi

Date:

Babban Bankin Najeriya CBN ya musanta rahotonnin da ke cewa gwamnan bankin Godwin Emefiele ya alaƙanta rashin wadatattun takardun buga sababbin kuɗi a ƙasa, kan ƙarancin takardun buga kuɗin.

Jaridar PREMIUM TIMES a ƙasar ce dai ta ruwaito wata majiya na shaida mata cewa Godwin Emefiele ya bayyana wa taron majalisar magabatan ƙasar cewa rashin isassun takardun buga kuɗi ne ya haddasa ƙarancin takardun sababbin kuɗin a ƙasar.

To amma a wata sanarwa da CBN ɗin ya fitar ya ce, babu inda gwamnan banki ya faɗi haka a lokacin da yake yi wa majalisar magabatan jawabi ranar Juma’a a fadar shugaban ƙasar.

Sanarwar ta ƙara da cewa abin da Mista Emefiele ya faɗa wa majalisar shi ne hukumar da ke lura da buga kuɗin na aikin buga kuɗin domin wadata ‘yan ƙasar da takardun kuɗin da suke buƙata domin harkokinsu na yau-da-kullum.

”Hukumar da ke Lura da Buga Kuɗi ta Ƙasa tana da isassun kayan aikin da take buƙata wajen buga sabbin kuɗin da za su wadatar. Dan haka CBN ke kira ga jama’a da su yi watsi da rahotonnin da ke cewa babu isassun takardun buga kuɗin tare da kiran jama’a su ƙara haƙuri, kasancewar muna bakin ƙoƙarinmu wajen ganin mun ƙara yawan kuɗin da ke yawo a hannun mutane”, in ji sanarwar.

Haka kuma sanarwar ta ce akwai wani sautin murya da ke yawo a shafukan sada zumunta wanda ke zargin cewa CBN na shirin rufe wasu bankuna, musamman a wasu yankunan.

Dan haka sanarwar ta ce CBN ba shi da wannan shiri, kuma saƙon da ke cikin muryar ya saɓa wa dokar tsarin banki na ƙasar.

Dan haka CBN ɗin ya shawarci ‘yan ƙasar da su yi watsi da saƙon sautin muryar kasancewar ba daga bankin yake ba.

legits news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp