fidelitybank

CBN ya baiwa Bankuna ƴancin sayar da dala a farashin da suke buƙata

Date:

Babban bankin ƙasa CBN, ya bai wa bankunan kasuwanci izinin yin musayar kudaden waje ta kowane farashi.

Izinin yana nufin cewa yanzu bankuna suna da ikon sayar da dala a ƙayyadaddun ƙimar kasuwa.

DAILY POST ta tattaro cewa wasu bankunan sun sanya darajar dalar Amurka zuwa Naira a kan N699 zuwa N750, lamarin da ke nuni da cewa a yanzu Najeriya na gudanar da canjin cikin ‘yanci daidai da alkawarin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi na farfaɗo da darajar Naira.

Da yake mayar da martani game da ci gaban a wata hira da gidan talabijin na Arise a ranar Laraba, Dr. Andrew Nevin,  Masanin Tattalin Arziki, ya ce hadewar farashin kudaden waje zai yi tasiri sosai a kasar ta hanyar bunkasa damar saka hannun jari a Najeriya.

“Abin da ke faruwa shi ne, CBN yana karbar daloli daga asusun tarayya yana baiwa masu hannu da shuni akan Naira 411 zuwa Dalar Amurka yayin da farashin dala ya kai N700 zuwa N750, a gaskiya ba mu sani ba saboda sun cire gaskiya.

“Abin da ya faru shi ne gwamnatin jihohi ba za ta iya biyan ‘yan fanshonsu ba. Wannan muhimmin al’amari za a magance shi ta hanyar ci gaba. Yanzu gwamnatin jihar za ta samu cikakken darajar dalar ta.

“Zai yi matukar tasiri a tsarin kasafin kudin kasar nan idan muka daina baiwa masu hannu da shuni dala. Muna samun ingantacciyar saka hannun jari, da yin amfani da albarkatun kasa na adalci da inganta yanayin kasuwanci, hakan zai karfafa kudin Najeriya,” inji shi.

Shekaru da dama, Najeriya ta ci gaba da sarrafa farashin musaya a hukumance yayin da kudaden da ake samu na kudin waje ya samu koma baya. Yayin da CBN ya ci gaba da samun kudin wucin gadi na $1/N462.

the sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp