fidelitybank

CBN ta yi bayanin ɓatan Naira biliyan 100 na kuɗin da suka lalace – SERAP

Date:

Ƙungiyar SERAP mai fafutikar yaƙi da cin hanci a Najeriya ta buƙaci gwamnan babban bankin ƙasar, Mista Olayemi Cardoso ya yi bayani kan ”yadda fiye da naira biliyan 100 na takardun kuɗin da suka lalace – da sauran kuɗi masu yawa da ke jiran tantancewa a rassan CBN ɗin – suka yi ɓatan dabo.

Cikin wata wasiƙa da ƙungiyar ta wallafa a shafnta na intanet, ta ce ta samu zarge-zargen ne cikin rahoton shekara-shekara da babban mai binciken kuɗi na ƙasa ya fitar a 2022.

“Rahoton babban mai binciken kuɗin na 2022 ya nuna cewa, tun a 2017 CBN ke ci gaba da taskance fiye da naira biliyan 100 na takardun kuɗin da suka lalace ko suka yi dauɗa, da wasu kuɗi masu yawa da ke jiran tantancewa a rassan CBN”.

Rahoton babban mai binciken kuɗin na fargabar cewa an karkatar, ko an sake maido da ”lalatattun takardun kuɗin da kuɗaɗen masu datti” da aka tsara cewa za a ƙone su.

Ƙungiyar ta ce zarge-zargen da ke cikin rahoton babban mai binciken kuɗin ya nuna yadda CBn din ya saɓa wa kundin tsarin mulki da dokar CBN da dokokin cin hanci na ƙasa da ma na duniya.

Haka kuma ƙungiyar ta kuma buƙaci gwamnan na CBN ya yi ƙarin haske ”kan inda naira biliyan 7.2 da aka ware domin gina resehn bankin a Dutse a shekarar 2010, da kuma naira biliyan 4.8 da aka ware don sabunta resehn CBN na birnin Abeokuta a shekarar 2009.

Serap ɗin ta kuma buƙaci CBN ya wallafa sunayen ‘yan kwangilar da aka bai wa ayyukan, kuma suka gaza aiwatar da su.

Ƙungiyar ta kuma ce CBN din ya yi wa jama’a bayani kan wasu basukan da bankin ya bai wa wasu jihohin ƙasar.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp