fidelitybank

CBN ta magantu a kan karanci kudi da ake fama da shi

Date:

Babban bankin Najeriya, CBN, ya ce isassun takardun kudi na Naira na yaduwa a yayin da ake samun rahotannin karancin kudaden.

A cikin wata sanarwa da Sashen Sadarwa na Kamfanin na CBN ya fitar, babban bankin ya bayyana dalilan da suka janyo karancin kudin Naira a wasu sassan kasar nan.

Matakin na CBN ya biyo bayan korafe-korafe da wasu abokan huldar bankuna ke yi kan karancin kudin da ake samu na Naira a kananun bankuna, Automated Teller Machines (ATMs), Points of Sale (PoS), da Bureaux de Change (BDCs).

Sai dai babban bankin ya ce ana ganin ana fama da karancin kudin ne sakamakon yadda bankunan Deposit Money Banks (DMBs) ke cire kudade daga rassa daban-daban na CBN.

Ya bayyana cewa janye firgici da abokan cinikin banki ke yi shi ma wani bangare ne ya haddasa karancin.

Babban bankin na CBN ya ce babu karancin kudin Naira, yana mai cewa akwai wadatattun kudaden a tattalin arzikin kasar.

“An jawo hankalin CBN akan rahotannin da ake zargin ana fama da karancin kudi a bankuna, ATMs, PoS da BDC a wasu manyan biranen kasar nan.

“Binciken da muka yi ya nuna cewa ana ganin karancin kudi a wasu wuraren ya samo asali ne saboda yawan cire kudi daga rassan CBN da DMBs suka yi da kuma firgita da kwastomomin da ke cirewa daga na’urar ATM.

“Yayin da muke lura da damuwar ‘yan Najeriya game da samar da tsabar kudi don hada-hadar kudi, muna so mu tabbatar wa jama’a cewa akwai isassun takardun kudi na ayyukan tattalin arziki a kasar,” in ji sanarwar.

www.legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp