fidelitybank

CBN na kan bakarta ba cire kudi a ATM – Emefiele

Date:

Babban bankin kasa, ya ce, babu gudu ba ja da baya a kan sabon tsarinsa na takaitawa É—aidaikun mutane cire kudi daga bankuna bayan kiraye-kiraye daga ko’ina a Najeriya cewar ya sake duba batun.

Gwamnan babban bankin, Godwin Emefiele ne ya bayyanawa manema labarai hakan a jiya Alhamis bayan ganawa da shugaba Muhammadu Buhari.

Ya ce batun da bankin zai sake dubawa shine adadin kudin da za a iya cirewa ba wai ya canja tsarin ba, inda ya ce sabon tsarin na nan daram.

Gwamnan babban bankin na magana ne bayan da majalisar wakilai ta nemi da a soke tsarin da kuma gayyatarsa zuwa gabanta domin ya yi mata bayani.

“Ina sane da batun jin karin bayani da ‘yan majalisa suka nema. Amma ina ganin abu mafi muhimmanci shi ne cewa tsarin ya faro ne tun a shekara ta 2012,” in ji Emefiele.

“Sai dai kusan sau uku zuwa hudu muna soke tsarin saboda muna ganin ya kamata mu yi kyakkyawan shiri da sake gyara tsarin biyan kudi a Najeriya.

”Tsakanin 2012 zuwa 2022, kusan shekara goma kenan, muna da yakinin cewa an samar da cibiyoyi na taimakawa mutane da dama yin hada-hadar kudaÉ—e a fadin kasa.

Emefiele ya ce akwai tsari da za a yi wa al’ummomi a karkara don tabbatar da cewa sabbin tsare-tsare ba su yi mummunan tasiri a kansu ba.

A ranar Talata ne, CBN ya taƙaita yawan kuɗade laƙadan da ƴan ƙasar za su iya cirewa daga asusun ajiyarsu na banki, inda yawan kuɗin da mutum ɗaya zai iya fitarwa a banki a sati shi ne naira 100,000 yayin da kamfani zai cire naira 500,000 ne kawai a sati.

mmm.nnn.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da É—anyen man kaÉ—anya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaÉ—a labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...

An gargadi Borno da Yobe da Jigawa su zama cikin shirin ambaliya

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da...

Kano na cikin jihohin da ba su yi katin zabe sosai ba – INEC

Bayanan da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya...

Mun gano filin wasa na Sani Abacha ba shi da inganci – NPFL

Hukumar shirya gasar cin kofin kwararru ta kasa (NPFL),...

Jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna ya ya fadi

Jirgin ƙasa ɗauke da fasinjoji da ya taso daga...

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: An yi wa Dan shekara 7 yankan Rago a Kano

Wasu ɓata gari da ba a san ko su...

Jami’in mu bai saci naira biliyan 6.5 ba – Gwamnatin Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahoton da ya zargi...
X whatsapp