Jamâiyyar PDP, dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bukaci babban bankin Najeriya, CBN, da ya sanya sunan tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo a kan takardun kudin Naira da aka sake fasalin.
Atiku ya ce ya kamata fuskar Obasanjo ta kasance a kan kudin Naira saboda kokarin da yake yi na ganin Najeriya ta zama wuri mai kyau.
Dan takarar shugaban kasa na PDP ya ce samun fuskar Obasanjo a naira zai kara zaburar da alâummar Najeriya nan gaba wajen sadaukarwa ga kasa.
A wani sako da ya wallafa a shafinsa na twitter, Atiku ya rubuta cewa: âAfrika ta yi albarka da samun shugaban kasa mai kishin dimokradiyya kamar Cif Obasanjo. Mutumin da ya kamata hotonsa ya kasance a cikin takardar naira da aka sake fasalin domin zaburar da alâummar Nijeriya gaba su sadaukar da kansu ga alâummarsu da nahiyarsu.â
A kwanakin baya ne gwamnan koli na bankin, Godwin Emefiele, ya sanar da sake fasalin kudin N100, N200, N500, da N1000.
Shugaban na CBN ya ce za a fitar da sabbin takardun ne a ranar 5 ga Disamba, 2022.