fidelitybank

CBN bai shirya ba kwata-kwata – Badaru

Date:

Gwamnan jihar Jigawa, Muhammad Badaru Abubakar, ya tunkari babban bankin Najeriya, CBN, a kan ci gaba da tabarbarewar kudaden Naira da aka yi wa kwaskwarima a bankunan kasuwanci.

Gwamnan ya bayyana hakan ne ta bakin kwamishinan kudi na jihar, Babangida Umar Gantsa a lokacin da yake mayar da martani kan wahalhalun da mutane ke ciki na saka ko cire kudaden su.

Ya zargi CBN da rike takardar kudin Naira da aka yi wa kwaskwarima, wanda hakan ya jawo wa ‘yan kasa kuncin da ba dole ba.

“Mun kuma yi magana da manajojin bankin, kuma sun tabbatar da cewa CBN ba ya ba su isassun kudi.

“Wani manajan wani banki ya shaida mana cewa CBN ya ba shi Naira miliyan biyu kacal.

“A cikin wani ATM na musamman, na kirga sama da mutane 250, mutane suna kwana a wurin wasu kuma suna kwashe sa’o’i na aikinsu don kawai su ciro kudi don bukatunsu. Bankunan ba sa loda isassun kudi a cikin ATM dinsu domin CBN ma ba ya ba su kudi.

“Ina ganin CBN bai shirya wannan atisayen ba. Kamata ya yi su koma kan allon zane su yi abin da ya dace don rage wa talaka radadin wahala.”

Karanta Wannan: Bullo da sababbin kudi ya dakile ta’addanci – CBN

Babangida ya kara da cewa, “har ma canjin naira da tsawaita kwanaki goma da CBN ta sanar za a yi nasara a kai.”

DAILY POST ta rahoto cewa, kananan hukumomi goma ne kawai cikin 27 da ke jihar ke da bankunan aiki.

Al’ummar karkara na cikin wahalhalun da ba za a iya mantawa da su ba domin ba su da damar samun wata cibiyar hada-hadar kudi don musanya tsohuwar takardar da tasu ta zamani da sababbi.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...
X whatsapp