fidelitybank

CBN bai ba mu isashshen kudi ba – Bankunan Kasuwanci

Date:

Bankunan kasuwanci sun mayar da martani kan iƙirarin babban bankin kasa CBN kan cewa, ya bai wa bankunan kasuwanci isassun sababbin kuɗaɗe kawai sun riƙe su ne.

Jaridar Solacebase ta ruwaito cewa, Mrs Hadiza Ambursa wadda jami’a ce a Access Bank, wadda ta wakilci manajan darakta ta ce, an ba su kashi 10 ne kacal cikin 100 na kuɗin da suka bai wa CBN.

A yayin wani zama da wakilan bankunan kasuwanci suka yi da kwamitin majalisar Najeriya, ma’aikaciyar ta ce “Ba ma samun kuɗin cikin gaggawa kamar yadda muke buƙata. Muna samun kashi 10 ne kawai cikin 100 na abin da muka kai wa CBN. Muna biya muna kuma karɓa kudi. Kuma a gefe ɗaya muna sanya kuɗin a ATM.

Mista Jimoh Garuba wanda wakilin Sterling Bank ne, yana samun kuɗi daga CBN amma ba ya kai wa yadda zai isa ga buƙatun kwastomominsa.

Yace, bankinsu na karɓar abin da bai gaza naira miliyan 150 ba daga CBN kowanne mako su rabawa reshinansu da ke Abuja.

Ya ƙara da cewa a Kaduna, bankinsu ya ƙarbi naira miliyan 150 a kowanne mako ya kuma raba su ga duka rassansa da ke jihohi 36 na tarayya.

Ya ce a Kano, “ana bamu naira miliyan 100 ne a mako, ba za mu iya komau da su ba bayan sanyawa a na’urar ATM”.

Ms Arerepade Akagwe, wadda wakilin United Bank for Africa (UBA) ne, ta ce ta karbi kashi 70 na tsofaffin kuɗin da ta bai wa CBN.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN akwai sauran bankuna irinsu Guarantee Trust Bank (GTB), ECO bank, Lotus Bank da Fidelity da suka amince sun karɓi kimanin kashi 60 na tsafaffin kuɗin da suka mayar wa CBN.

Shugaban kwamitin ɗan majalisar wakilai alhassan Ado-Doguwa ya ce gayyatar da aka yi wa bankunan ba abin ta da jijiyar wuya ba ne, yanayi ne na bincike kan abin da ya shafi al’umar Najeriya.

“Muna da buƙatar sanin gaskiya kan ainihin iƙirarin da bankunan kasuwanci suke yi na cewa CBN bai bayar da sabbin kuɗi ba, da kuma na CBN da ke cewa ya bayar da kudaden da suka kamata.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp