Wani fashewa ya afku a bututun Trans-Niger a Bodo, karamar hukumar Gokana ta jihar Ribas.
Fashewar ta afku ne da yammacin jiya Litinin a kusa da hanyar Bodo zuwa Bonny, wadda ake kan ginawa a halin yanzu.
Har yanzu dai yankin da abin ya shafa na babban bututun na ci gaba da cin wuta, ko da yake har yanzu ba a san ainihin musabbabin fashewar ba.
Kawo yanzu dai babu tabbas ko lamarin ya samo asali ne daga tsoma bakin mutane musamman a dai dai lokacin da kungiyoyin ‘yan ta’adda suka yi barazanar kai hari a cibiyoyin mai.
Wadannan barazanar sun samo asali ne daga yadda Gwamnatin Tarayya ta hana kason Jihar Ribas saboda rikicin siyasa da ake fama da shi.
TNP, wani muhimmin layin jigilar mai na gwamnatin tarayya, yana samar da danyen mai zuwa tashar fitar da man fetur ta Bonny dake jihar Rivers.
Fashewar ta haifar da damuwa game da yiwuwar lalacewar muhalli da kuma kawo cikas ga samar da mai a yankin.
Har yanzu hukumomin gwamnati ba su fitar da wata sanarwa dangane da lamarin ba.