fidelitybank

Burtaniya ta sanya wa Iran takunkumi

Date:

Burtaniya ta sanar da saka jerin takunkumi kan wasu manyan sojojin ƙasar Iran da ƙungiyoyi sakamakon harin da Iran ɗin ta kai wa Isra’ila ranar 1 ga watan Okotoba.

Mutanen da takunkumin ya shafa sun haɗa da Abdol Rahim Mousavi, wanda kwamanda ne na sojojin Iran sannan kuma mamba na majalisar ƙoli ta tsaro ta Iran da kuma Hamid Vahedi wanda shi kuma kwamanda a rundunar sojin saman na Iran.

Mutanen da aka sanyawa takunkuman za su fuskanci haramci tafiye-tafiye da kuma hana su amfani da kuɗaɗensu, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen Burtaniyar ta sanar.

Hukumar kula da sararin samaniyyar ƙasar Iran wadda ke ƙera fasahohin da ake amfani wajen ƙera makamai masu linzami da ke gudun ƙifta ido, ita ma takunkumin ya shafe ta ta hanyar hana ta amfani da kuɗaɗ da kadarori. In ji BBC.

A ranar 1 ga watan oktoba ne dai Iran ɗin ta ƙaddamar da hari a kan Isra’ila inda ta aike da makamai masu linzami masu gudun kiftawa da Bisimilla fiye da 180.

Sojojin Isra’ila sun ce sun kama mafi yawan makaman.

today nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp