Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ka iya fuskantar kamu idan ya shiga Birtaniya, bayan hukuncin Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta ICC na bayar da sammacin kama shi, kamar yadda fadar gwamnatin Birtaniyar ta nuna.
Mai magana da yawun firaministan Birtaniya, ya ƙi yin magana game da shari’ar, amma ya ce gwamnati za ta sauke ”nauyin da shari’a” ta ɗora mata.
A ranar Alhamis ne Kotun ICC ta bayar da sammacin kama Netanyahu tare da tsohon ministan tsaron ƙasar, Yoav Gallant, kan zargin aikata laifukan yaƙi a Gaza.
Duka ƙasashe mambobin kotun, ciki har da Birtaniya, sun sanya hannun kan yarjejeniyar da ta ɗora musu alhakin aiwatar da sammacin kamu da kotun ta bayar kan ko wane ne.
Da aka tambaye shi ko za a tsare Netanyahu idan ya shiga Birtaniya, kakakin firaministan na Birtaniya bai ce komai ba kan batun.
To amma ya ce ”gwamnati za ta sauke nauyin shari’a da ke kanta ƙarƙashin dokokin da shari’a ta gindaya”.