fidelitybank

Burtaniya borin kunya kawai ta ke yi ɗan takarar su ya sha kayi – Kayode

Date:

Femi Fani-Kayode, jigo a jam’iyyar All Progressives Congress, APC, ya caccaki mataimakin babban kwamishinan Biritaniya a Najeriya, Ben Llewellyn-Jones kan wani kalami a kansa.

A ranar Lahadin da ta gabata ne jakadan Burtaniya, ya tunkari Fani-Kayode kan kalamansa na tunzura jama’a a shafukan sada zumunta.

A wata hira da ya yi da gidan rediyon Najeriya Info FM a ranar Lahadi, Llewellyn-Jones ya bayyana damuwarsa kan yadda za a iya haifar da kalaman batanci da tsohon ministan sufurin jiragen sama ke yi kan jam’iyyun adawa.

Da yake mayar da martani, FFK, a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter, ya bukaci wakilin Burtaniya da ya kaucewa al’amuran Najeriya, yana mai cewa kasar ba ta mulkin mallaka ba ce.

A cewar tsohon ministan, dan takarar da aka fi so na wakilin Birtaniya ya sha kaye a zaben shugaban kasa da aka kammala.

Ya rubuta cewa, “Zan shawarci wannan Ben, wanda aka ce min shi ne mataimakin babban kwamishinan Burtaniya a Najeriya, da ya kiyaye dattin hancinsa daga cikin harkokinmu na cikin gida.

“Na san cewa dan takarar da ya fi so bai ci zaben shugaban kasa ba, amma hakan ba yana nufin ya tsallaka layi ya dauki ‘yanci tare da mu a nan ba. Ina mamakin wanda yake tunanin shi ne?”

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp