Mutum takwas ne suka mutu bayan sun sha burkutu a birnin Bandar Abbas na kasar Iran, a cewar kafafen watsa labaran kasar.
Kazalika an kwantar da mutum 51 a asibiti sakamakon shan burkutun, kamar yadda wata jami’iar lafiya a birnin Dr Fatemeh Nowruzian ta shaida wa taron manema labarai.
Mutum 17 daga cikinsu suna halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai, yayin da aka yi wa mutum 30 wankin-koda, in ji likitar.
‘Yan-sanda sun ce sun kama mutum takwas bisa zargin yin burkutun da kuma raba ta ga jama’a.
Kasar Iran ta haramta yin barasa da sayar da ita da kuma shan ta, ko da yake ana barin wasu da ba Msulmai ba su sha.
Ana yi wa dukkan Musulmin da aka samu da lafin shan barasa bulala 80. A cewar BBC.