fidelitybank

Burkina Faso ta kori jami’an Faransa daga kasar ta

Date:

Burkina Faso ta kori jami’an diflomasiyya uku saboda neman tayar da ƙayar baya, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen ƙasar ta shaida cikin sanarwar da ta aike wa Faransa.

Sanarwar na ɗauke da kwanan watan 16 ga watan Afrilu sai dai ba ta yi cikakken bayani kan ayyukan da jami’an suka yi ba.

An buƙaci jami’an diflomasiyyar da suka haɗa da mashawarta kan harkokin siyasa biyu a ofishin jakadancin Faransa a Ouagadougou, su fice daga Burkina Faso cikin sa’a 48,” in ji sanarwar.

Alaƙa tsakanin Burkina Faso da Faransa – ƙasar da ta mulke ta a baya ta yi tsami tun da Kyaftin Ibrahim Traore ya ƙwace mulki a juyin mulkin da aka yi a Satumbar 2022.

Shugaban sojin da ke mulki ya karkatar da alaƙar Burkina Faso ga Rasha tare da kawo ƙarshen kusancinsu da Faransa.

A ƙarƙashin mulkinsa, an kori jami’an diflomasiyyar Faransa da dama kuma an rufe sansanin sojojin Faransa da ke ƙasar.

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp