fidelitybank

Burkina Faso ta kori jami’an Faransa daga kasar ta

Date:

Burkina Faso ta kori jami’an diflomasiyya uku saboda neman tayar da ƙayar baya, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen ƙasar ta shaida cikin sanarwar da ta aike wa Faransa.

Sanarwar na ɗauke da kwanan watan 16 ga watan Afrilu sai dai ba ta yi cikakken bayani kan ayyukan da jami’an suka yi ba.

An buƙaci jami’an diflomasiyyar da suka haɗa da mashawarta kan harkokin siyasa biyu a ofishin jakadancin Faransa a Ouagadougou, su fice daga Burkina Faso cikin sa’a 48,” in ji sanarwar.

Alaƙa tsakanin Burkina Faso da Faransa – ƙasar da ta mulke ta a baya ta yi tsami tun da Kyaftin Ibrahim Traore ya ƙwace mulki a juyin mulkin da aka yi a Satumbar 2022.

Shugaban sojin da ke mulki ya karkatar da alaƙar Burkina Faso ga Rasha tare da kawo ƙarshen kusancinsu da Faransa.

A ƙarƙashin mulkinsa, an kori jami’an diflomasiyyar Faransa da dama kuma an rufe sansanin sojojin Faransa da ke ƙasar.

benue news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Har yanzu Tinubu bai nada Jakadun Najeriya ba – ADC

Jam’iyyar ADC ta soki yadda gwamnatin APC ta shugaba...

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...
X whatsapp